aip_quran
Translation

  العربية              Hausa 

1. Surah Al-Fatiha
2. Surah Al-Baqara
3. Surah Aal-e-Imran
4. Surah An-Nisa
5. Surah Al-Maidah
6. Surah Al-Anam
7. Surah Al-Araf
8. Surah Al-Anfal
9. Surah At-Tawbah
10. Surah Yunus
11. Surah Hud
12. Surah Yusuf
13. Surah Ar-Rad
14. Surah Ibrahim
15. Surah Al-Hijr
16. Surah An-Nahl
17. Surah Al-Isra
18. Surah Al-Kahf
19. Surah Maryam
20. Surah Taha
21. Surah Al-Anbiya
22. Surah Al-Hajj
23. Surah Al-Muminun
24. Surah An-Nur
25. Surah Al-Furqan
26. Surah Ash-Shuara
27. Surah An-Naml
28. Surah Al-Qasas
29. Surah Al-Ankabut
30. Surah Ar-Rum
31. Surah Luqman
32. Surah As-Sajdah
33. Surah Al-Ahzab
34. Surah Saba
35. Surah Fatir
36. Surah Ya-Sin
37. Surah As-Saffat
38. Surah Sad
39. Surah Az-Zumar
40. Surah Ghafir
41. Surah Fussilat
42. Surah Ash-Shuraa
43. Surah Az-Zukhruf
44. Surah Ad-Dukhan
45. Surah Al-Jathiya
46. Surah Al-Ahqaf
47. Surah Muhammad
48. Surah Al-Fath
49. Surah Al-Hujurat
50. Surah Qaf
51. Surah Adh-Dhariyat
52. Surah At-Tur
53. Surah An-Najm
54. Surah Al-Qamar
55. Surah Ar-Rahman
56. Surah Al-Waqiah
57. Surah Al-Hadid
58. Surah Al-Mujadila
59. Surah Al-Hashr
60. Surah Al-Mumtahanah
61. Surah As-Saf
62. Surah Al-Jumuah
63. Surah Al-Munafiqun
64. Surah Al-Taghabun
65. Surah At-Talaq
66. Surah At-Tahrim
67. Surah Al-Mulk
68. Surah Al-Qalam
69. Surah Al-Haqqah
70. Surah Al-Maarij
71. Surah Nuh
72. Surah Al-Jinn
73. Surah Al-Muzzammil
74. Surah Al-Muddaththir
75. Surah Al-Qiyamah
76. Surah Al-Insan
77. Surah Al-Mursalat
78. Surah An-Naba
79. Surah An-Naziat
80. Surah Abasa
81. Surah At-Takwir
82. Surah Al-Infitar
83. Surah Al-Mutaffifin
84. Surah Al-Inshiqaq
85. Surah Al-Buruj
86. Surah At-Tariq
87. Surah Al-Ala
88. Surah Al-Ghashiyah
89. Surah Al-Fajr
90. Surah Al-Balad
91. Surah Ash-Shams
92. Surah Al-Layl
93. Surah Ad-Duhaa
94. Surah Ash-Sharh
95. Surah At-Tin
96. Surah Al-Alaq
97. Surah Al-Qadr
98. Surah Al-Bayyinah
99. Surah Az-Zalzalah
100. Surah Al-Adiyat
101. Surah Al-Qariah
102. Surah At-Takathur
103. Surah Al-Asr
104. Surah Al-Humazah
105. Surah Al-Fil
106. Surah Quraysh
107. Surah Al-Maun
108. Surah Al-Kawthar
109. Surah Al-Kafirun
110. Surah An-Nasr
111. Surah Al-Masad
112. Surah Al-Ikhlas
113. Surah Al-Falaq
114. Surah An-Nas

70. Surah Al-Maarij

70:1  سَأَلَ سَائِلٌ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
70:2  لِّلْكَافِرِينَ لَيْسَ لَهُ دَافِعٌ
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
70:3  مِّنَ اللَّهِ ذِي الْمَعَارِجِ
Daga Allah Mai matãkala.
70:4  تَعْرُجُ الْمَلَائِكَةُ وَالرُّوحُ إِلَيْهِ فِي يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
70:5  فَاصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلًا
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
70:6  إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُ بَعِيدًا
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
70:7  وَنَرَاهُ قَرِيبًا
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
70:8  يَوْمَ تَكُونُ السَّمَاءُ كَالْمُهْلِ
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
70:9  وَتَكُونُ الْجِبَالُ كَالْعِهْنِ
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
70:10  وَلَا يَسْأَلُ حَمِيمٌ حَمِيمًا
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
70:11  يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ الْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِي مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍ بِبَنِيهِ
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
70:12  وَصَاحِبَتِهِ وَأَخِيهِ
Da matarsa da ɗan'uwansa.
70:13  وَفَصِيلَتِهِ الَّتِي تُؤْوِيهِ
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
70:14  وَمَن فِي الْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
70:15  كَلَّا ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
70:16  نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىٰ
Mai twãle fãtar goshi.
70:17  تَدْعُو مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
70:18  وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰ
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
70:19  إِنَّ الْإِنسَانَ خُلِقَ هَلُوعًا
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
70:20  إِذَا مَسَّهُ الشَّرُّ جَزُوعًا
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
70:21  وَإِذَا مَسَّهُ الْخَيْرُ مَنُوعًا
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
70:22  إِلَّا الْمُصَلِّينَ
Sai mãsu yin salla,
70:23  الَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَائِمُونَ
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
70:24  وَالَّذِينَ فِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
70:25  لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِ
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
70:26  وَالَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ الدِّينِ
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
70:27  وَالَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
70:28  إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
70:29  وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
70:30  إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
70:31  فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُونَ
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
70:32  وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَ
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
70:33  وَالَّذِينَ هُم بِشَهَادَاتِهِمْ قَائِمُونَ
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
70:34  وَالَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
70:35  أُولَٰئِكَ فِي جَنَّاتٍ مُّكْرَمُونَ
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
70:36  فَمَالِ الَّذِينَ كَفَرُوا قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
70:37  عَنِ الْيَمِينِ وَعَنِ الشِّمَالِ عِزِينَ
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
70:38  أَيَطْمَعُ كُلُّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
70:39  كَلَّا ۖ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
70:40  فَلَا أُقْسِمُ بِرَبِّ الْمَشَارِقِ وَالْمَغَارِبِ إِنَّا لَقَادِرُونَ
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
70:41  عَلَىٰ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
70:42  فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا وَيَلْعَبُوا حَتَّىٰ يُلَاقُوا يَوْمَهُمُ الَّذِي يُوعَدُونَ
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
70:43  يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ الْأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍ يُوفِضُونَ
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
70:44  خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۚ ذَٰلِكَ الْيَوْمُ الَّذِي كَانُوا يُوعَدُونَ
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)