aip_quran
Translation

  العربية              Hausa 

1. Surah Al-Fatiha
2. Surah Al-Baqara
3. Surah Aal-e-Imran
4. Surah An-Nisa
5. Surah Al-Maidah
6. Surah Al-Anam
7. Surah Al-Araf
8. Surah Al-Anfal
9. Surah At-Tawbah
10. Surah Yunus
11. Surah Hud
12. Surah Yusuf
13. Surah Ar-Rad
14. Surah Ibrahim
15. Surah Al-Hijr
16. Surah An-Nahl
17. Surah Al-Isra
18. Surah Al-Kahf
19. Surah Maryam
20. Surah Taha
21. Surah Al-Anbiya
22. Surah Al-Hajj
23. Surah Al-Muminun
24. Surah An-Nur
25. Surah Al-Furqan
26. Surah Ash-Shuara
27. Surah An-Naml
28. Surah Al-Qasas
29. Surah Al-Ankabut
30. Surah Ar-Rum
31. Surah Luqman
32. Surah As-Sajdah
33. Surah Al-Ahzab
34. Surah Saba
35. Surah Fatir
36. Surah Ya-Sin
37. Surah As-Saffat
38. Surah Sad
39. Surah Az-Zumar
40. Surah Ghafir
41. Surah Fussilat
42. Surah Ash-Shuraa
43. Surah Az-Zukhruf
44. Surah Ad-Dukhan
45. Surah Al-Jathiya
46. Surah Al-Ahqaf
47. Surah Muhammad
48. Surah Al-Fath
49. Surah Al-Hujurat
50. Surah Qaf
51. Surah Adh-Dhariyat
52. Surah At-Tur
53. Surah An-Najm
54. Surah Al-Qamar
55. Surah Ar-Rahman
56. Surah Al-Waqiah
57. Surah Al-Hadid
58. Surah Al-Mujadila
59. Surah Al-Hashr
60. Surah Al-Mumtahanah
61. Surah As-Saf
62. Surah Al-Jumuah
63. Surah Al-Munafiqun
64. Surah Al-Taghabun
65. Surah At-Talaq
66. Surah At-Tahrim
67. Surah Al-Mulk
68. Surah Al-Qalam
69. Surah Al-Haqqah
70. Surah Al-Maarij
71. Surah Nuh
72. Surah Al-Jinn
73. Surah Al-Muzzammil
74. Surah Al-Muddaththir
75. Surah Al-Qiyamah
76. Surah Al-Insan
77. Surah Al-Mursalat
78. Surah An-Naba
79. Surah An-Naziat
80. Surah Abasa
81. Surah At-Takwir
82. Surah Al-Infitar
83. Surah Al-Mutaffifin
84. Surah Al-Inshiqaq
85. Surah Al-Buruj
86. Surah At-Tariq
87. Surah Al-Ala
88. Surah Al-Ghashiyah
89. Surah Al-Fajr
90. Surah Al-Balad
91. Surah Ash-Shams
92. Surah Al-Layl
93. Surah Ad-Duhaa
94. Surah Ash-Sharh
95. Surah At-Tin
96. Surah Al-Alaq
97. Surah Al-Qadr
98. Surah Al-Bayyinah
99. Surah Az-Zalzalah
100. Surah Al-Adiyat
101. Surah Al-Qariah
102. Surah At-Takathur
103. Surah Al-Asr
104. Surah Al-Humazah
105. Surah Al-Fil
106. Surah Quraysh
107. Surah Al-Maun
108. Surah Al-Kawthar
109. Surah Al-Kafirun
110. Surah An-Nasr
111. Surah Al-Masad
112. Surah Al-Ikhlas
113. Surah Al-Falaq
114. Surah An-Nas

69. Surah Al-Haqqah

69:1  الْحَاقَّةُ
Kiran gaskiya!
69:2  مَا الْحَاقَّةُ
Mẽne ne kiran gaskiya?
69:3  وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحَاقَّةُ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
69:4  كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌ بِالْقَارِعَةِ
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
69:5  فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا بِالطَّاغِيَةِ
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
69:6  وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
69:7  سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَانِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
69:8  فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّن بَاقِيَةٍ
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
69:9  وَجَاءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُ وَالْمُؤْتَفِكَاتُ بِالْخَاطِئَةِ
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
69:10  فَعَصَوْا رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
69:11  إِنَّا لَمَّا طَغَى الْمَاءُ حَمَلْنَاكُمْ فِي الْجَارِيَةِ
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
69:12  لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَا أُذُنٌ وَاعِيَةٌ
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
69:13  فَإِذَا نُفِخَ فِي الصُّورِ نَفْخَةٌ وَاحِدَةٌ
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
69:14  وَحُمِلَتِ الْأَرْضُ وَالْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَاحِدَةً
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
69:15  فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
69:16  وَانشَقَّتِ السَّمَاءُ فَهِيَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
69:17  وَالْمَلَكُ عَلَىٰ أَرْجَائِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَانِيَةٌ
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
69:18  يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
69:19  فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ فَيَقُولُ هَاؤُمُ اقْرَءُوا كِتَابِيَهْ
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
69:20  إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَاقٍ حِسَابِيَهْ
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
69:21  فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
69:22  فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
69:23  قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
69:24  كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا أَسْلَفْتُمْ فِي الْأَيَّامِ الْخَالِيَةِ
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
69:25  وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِشِمَالِهِ فَيَقُولُ يَا لَيْتَنِي لَمْ أُوتَ كِتَابِيَهْ
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
69:26  وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
69:27  يَا لَيْتَهَا كَانَتِ الْقَاضِيَةَ
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
69:28  مَا أَغْنَىٰ عَنِّي مَالِيَهْ ۜ
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
69:29  هَلَكَ عَنِّي سُلْطَانِيَهْ
"Ĩkona ya ɓace mini!"
69:30  خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
69:31  ثُمَّ الْجَحِيمَ صَلُّوهُ
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
69:32  ثُمَّ فِي سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَاسْلُكُوهُ
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
69:33  إِنَّهُ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِاللَّهِ الْعَظِيمِ
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
69:34  وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
69:35  فَلَيْسَ لَهُ الْيَوْمَ هَاهُنَا حَمِيمٌ
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
69:36  وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
69:37  لَّا يَأْكُلُهُ إِلَّا الْخَاطِئُونَ
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
69:38  فَلَا أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
69:39  وَمَا لَا تُبْصِرُونَ
Da abin da bã ku iya gani.
69:40  إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
69:41  وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
69:42  وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
69:43  تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَ
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
69:44  وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ الْأَقَاوِيلِ
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
69:45  لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِالْيَمِينِ
Dã Mun kãma shi da dãma.
69:46  ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ الْوَتِينَ
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
69:47  فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَاجِزِينَ
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
69:48  وَإِنَّهُ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
69:49  وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
69:50  وَإِنَّهُ لَحَسْرَةٌ عَلَى الْكَافِرِينَ
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
69:51  وَإِنَّهُ لَحَقُّ الْيَقِينِ
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
69:52  فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.