aip_quran
Translation

  العربية              Hausa 

1. Surah Al-Fatiha
2. Surah Al-Baqara
3. Surah Aal-e-Imran
4. Surah An-Nisa
5. Surah Al-Maidah
6. Surah Al-Anam
7. Surah Al-Araf
8. Surah Al-Anfal
9. Surah At-Tawbah
10. Surah Yunus
11. Surah Hud
12. Surah Yusuf
13. Surah Ar-Rad
14. Surah Ibrahim
15. Surah Al-Hijr
16. Surah An-Nahl
17. Surah Al-Isra
18. Surah Al-Kahf
19. Surah Maryam
20. Surah Taha
21. Surah Al-Anbiya
22. Surah Al-Hajj
23. Surah Al-Muminun
24. Surah An-Nur
25. Surah Al-Furqan
26. Surah Ash-Shuara
27. Surah An-Naml
28. Surah Al-Qasas
29. Surah Al-Ankabut
30. Surah Ar-Rum
31. Surah Luqman
32. Surah As-Sajdah
33. Surah Al-Ahzab
34. Surah Saba
35. Surah Fatir
36. Surah Ya-Sin
37. Surah As-Saffat
38. Surah Sad
39. Surah Az-Zumar
40. Surah Ghafir
41. Surah Fussilat
42. Surah Ash-Shuraa
43. Surah Az-Zukhruf
44. Surah Ad-Dukhan
45. Surah Al-Jathiya
46. Surah Al-Ahqaf
47. Surah Muhammad
48. Surah Al-Fath
49. Surah Al-Hujurat
50. Surah Qaf
51. Surah Adh-Dhariyat
52. Surah At-Tur
53. Surah An-Najm
54. Surah Al-Qamar
55. Surah Ar-Rahman
56. Surah Al-Waqiah
57. Surah Al-Hadid
58. Surah Al-Mujadila
59. Surah Al-Hashr
60. Surah Al-Mumtahanah
61. Surah As-Saf
62. Surah Al-Jumuah
63. Surah Al-Munafiqun
64. Surah Al-Taghabun
65. Surah At-Talaq
66. Surah At-Tahrim
67. Surah Al-Mulk
68. Surah Al-Qalam
69. Surah Al-Haqqah
70. Surah Al-Maarij
71. Surah Nuh
72. Surah Al-Jinn
73. Surah Al-Muzzammil
74. Surah Al-Muddaththir
75. Surah Al-Qiyamah
76. Surah Al-Insan
77. Surah Al-Mursalat
78. Surah An-Naba
79. Surah An-Naziat
80. Surah Abasa
81. Surah At-Takwir
82. Surah Al-Infitar
83. Surah Al-Mutaffifin
84. Surah Al-Inshiqaq
85. Surah Al-Buruj
86. Surah At-Tariq
87. Surah Al-Ala
88. Surah Al-Ghashiyah
89. Surah Al-Fajr
90. Surah Al-Balad
91. Surah Ash-Shams
92. Surah Al-Layl
93. Surah Ad-Duhaa
94. Surah Ash-Sharh
95. Surah At-Tin
96. Surah Al-Alaq
97. Surah Al-Qadr
98. Surah Al-Bayyinah
99. Surah Az-Zalzalah
100. Surah Al-Adiyat
101. Surah Al-Qariah
102. Surah At-Takathur
103. Surah Al-Asr
104. Surah Al-Humazah
105. Surah Al-Fil
106. Surah Quraysh
107. Surah Al-Maun
108. Surah Al-Kawthar
109. Surah Al-Kafirun
110. Surah An-Nasr
111. Surah Al-Masad
112. Surah Al-Ikhlas
113. Surah Al-Falaq
114. Surah An-Nas

68. Surah Al-Qalam

68:1  ن ۚ وَالْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
68:2  مَا أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍ
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
68:3  وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍ
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
68:4  وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
68:5  فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
68:6  بِأَييِّكُمُ الْمَفْتُونُ
Ga wanenku haukã take.
68:7  إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِالْمُهْتَدِينَ
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
68:8  فَلَا تُطِعِ الْمُكَذِّبِينَ
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
68:9  وَدُّوا لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
68:10  وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
68:11  هَمَّازٍ مَّشَّاءٍ بِنَمِيمٍ
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
68:12  مَّنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
68:13  عُتُلٍّ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
68:14  أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
68:15  إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
68:16  سَنَسِمُهُ عَلَى الْخُرْطُومِ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
68:17  إِنَّا بَلَوْنَاهُمْ كَمَا بَلَوْنَا أَصْحَابَ الْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
68:18  وَلَا يَسْتَثْنُونَ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
68:19  فَطَافَ عَلَيْهَا طَائِفٌ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَائِمُونَ
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
68:20  فَأَصْبَحَتْ كَالصَّرِيمِ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
68:21  فَتَنَادَوْا مُصْبِحِينَ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
68:22  أَنِ اغْدُوا عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَارِمِينَ
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
68:23  فَانطَلَقُوا وَهُمْ يَتَخَافَتُونَ
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
68:24  أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا الْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌ
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
68:25  وَغَدَوْا عَلَىٰ حَرْدٍ قَادِرِينَ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
68:26  فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوا إِنَّا لَضَالُّونَ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
68:27  بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
68:28  قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
68:29  قَالُوا سُبْحَانَ رَبِّنَا إِنَّا كُنَّا ظَالِمِينَ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
68:30  فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَلَاوَمُونَ
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
68:31  قَالُوا يَا وَيْلَنَا إِنَّا كُنَّا طَاغِينَ
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
68:32  عَسَىٰ رَبُّنَا أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًا مِّنْهَا إِنَّا إِلَىٰ رَبِّنَا رَاغِبُونَ
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
68:33  كَذَٰلِكَ الْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ الْآخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا يَعْلَمُونَ
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
68:34  إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّاتِ النَّعِيمِ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
68:35  أَفَنَجْعَلُ الْمُسْلِمِينَ كَالْمُجْرِمِينَ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
68:36  مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
68:37  أَمْ لَكُمْ كِتَابٌ فِيهِ تَدْرُسُونَ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
68:38  إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
68:39  أَمْ لَكُمْ أَيْمَانٌ عَلَيْنَا بَالِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ الْقِيَامَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
68:40  سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
68:41  أَمْ لَهُمْ شُرَكَاءُ فَلْيَأْتُوا بِشُرَكَائِهِمْ إِن كَانُوا صَادِقِينَ
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
68:42  يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍ وَيُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
68:43  خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۖ وَقَدْ كَانُوا يُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ وَهُمْ سَالِمُونَ
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
68:44  فَذَرْنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا الْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
68:45  وَأُمْلِي لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِي مَتِينٌ
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
68:46  أَمْ تَسْأَلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَ
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
68:47  أَمْ عِندَهُمُ الْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
68:48  فَاصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ الْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌ
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
68:49  لَّوْلَا أَن تَدَارَكَهُ نِعْمَةٌ مِّن رَّبِّهِ لَنُبِذَ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ مَذْمُومٌ
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
68:50  فَاجْتَبَاهُ رَبُّهُ فَجَعَلَهُ مِنَ الصَّالِحِينَ
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
68:51  وَإِن يَكَادُ الَّذِينَ كَفَرُوا لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَارِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا الذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُ لَمَجْنُونٌ
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
68:52  وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.