aip_quran
Translation

  العربية              Hausa 

1. Surah Al-Fatiha
2. Surah Al-Baqara
3. Surah Aal-e-Imran
4. Surah An-Nisa
5. Surah Al-Maidah
6. Surah Al-Anam
7. Surah Al-Araf
8. Surah Al-Anfal
9. Surah At-Tawbah
10. Surah Yunus
11. Surah Hud
12. Surah Yusuf
13. Surah Ar-Rad
14. Surah Ibrahim
15. Surah Al-Hijr
16. Surah An-Nahl
17. Surah Al-Isra
18. Surah Al-Kahf
19. Surah Maryam
20. Surah Taha
21. Surah Al-Anbiya
22. Surah Al-Hajj
23. Surah Al-Muminun
24. Surah An-Nur
25. Surah Al-Furqan
26. Surah Ash-Shuara
27. Surah An-Naml
28. Surah Al-Qasas
29. Surah Al-Ankabut
30. Surah Ar-Rum
31. Surah Luqman
32. Surah As-Sajdah
33. Surah Al-Ahzab
34. Surah Saba
35. Surah Fatir
36. Surah Ya-Sin
37. Surah As-Saffat
38. Surah Sad
39. Surah Az-Zumar
40. Surah Ghafir
41. Surah Fussilat
42. Surah Ash-Shuraa
43. Surah Az-Zukhruf
44. Surah Ad-Dukhan
45. Surah Al-Jathiya
46. Surah Al-Ahqaf
47. Surah Muhammad
48. Surah Al-Fath
49. Surah Al-Hujurat
50. Surah Qaf
51. Surah Adh-Dhariyat
52. Surah At-Tur
53. Surah An-Najm
54. Surah Al-Qamar
55. Surah Ar-Rahman
56. Surah Al-Waqiah
57. Surah Al-Hadid
58. Surah Al-Mujadila
59. Surah Al-Hashr
60. Surah Al-Mumtahanah
61. Surah As-Saf
62. Surah Al-Jumuah
63. Surah Al-Munafiqun
64. Surah Al-Taghabun
65. Surah At-Talaq
66. Surah At-Tahrim
67. Surah Al-Mulk
68. Surah Al-Qalam
69. Surah Al-Haqqah
70. Surah Al-Maarij
71. Surah Nuh
72. Surah Al-Jinn
73. Surah Al-Muzzammil
74. Surah Al-Muddaththir
75. Surah Al-Qiyamah
76. Surah Al-Insan
77. Surah Al-Mursalat
78. Surah An-Naba
79. Surah An-Naziat
80. Surah Abasa
81. Surah At-Takwir
82. Surah Al-Infitar
83. Surah Al-Mutaffifin
84. Surah Al-Inshiqaq
85. Surah Al-Buruj
86. Surah At-Tariq
87. Surah Al-Ala
88. Surah Al-Ghashiyah
89. Surah Al-Fajr
90. Surah Al-Balad
91. Surah Ash-Shams
92. Surah Al-Layl
93. Surah Ad-Duhaa
94. Surah Ash-Sharh
95. Surah At-Tin
96. Surah Al-Alaq
97. Surah Al-Qadr
98. Surah Al-Bayyinah
99. Surah Az-Zalzalah
100. Surah Al-Adiyat
101. Surah Al-Qariah
102. Surah At-Takathur
103. Surah Al-Asr
104. Surah Al-Humazah
105. Surah Al-Fil
106. Surah Quraysh
107. Surah Al-Maun
108. Surah Al-Kawthar
109. Surah Al-Kafirun
110. Surah An-Nasr
111. Surah Al-Masad
112. Surah Al-Ikhlas
113. Surah Al-Falaq
114. Surah An-Nas

56. Surah Al-Waqiah

56:1  إِذَا وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ
Idan mai aukuwa ta auku.
56:2  لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ
Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.
56:3  خَافِضَةٌ رَّافِعَةٌ
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
56:4  إِذَا رُجَّتِ الْأَرْضُ رَجًّا
Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.
56:5  وَبُسَّتِ الْجِبَالُ بَسًّا
Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.
56:6  فَكَانَتْ هَبَاءً مُّنبَثًّا
Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.
56:7  وَكُنتُمْ أَزْوَاجًا ثَلَاثَةً
Kuma kun kasance nau'i uku.
56:8  فَأَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ مَا أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ
Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
56:9  وَأَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ مَا أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ
Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?
56:10  وَالسَّابِقُونَ السَّابِقُونَ
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
56:11  أُولَٰئِكَ الْمُقَرَّبُونَ
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
56:12  فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ
A ckin Aljannar ni'ima.
56:13  ثُلَّةٌ مِّنَ الْأَوَّلِينَ
Jama'a ne daga mutãnen farko.
56:14  وَقَلِيلٌ مِّنَ الْآخِرِينَ
Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.
56:15  عَلَىٰ سُرُرٍ مَّوْضُونَةٍ
(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.
56:16  مُّتَّكِئِينَ عَلَيْهَا مُتَقَابِلِينَ
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
56:17  يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَانٌ مُّخَلَّدُونَ
Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.
56:18  بِأَكْوَابٍ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ
Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.
56:19  لَّا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنزِفُونَ
Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.
56:20  وَفَاكِهَةٍ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
56:21  وَلَحْمِ طَيْرٍ مِّمَّا يَشْتَهُونَ
Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.
56:22  وَحُورٌ عِينٌ
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
56:23  كَأَمْثَالِ اللُّؤْلُؤِ الْمَكْنُونِ
Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.
56:24  جَزَاءً بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
56:25  لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا تَأْثِيمًا
Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.
56:26  إِلَّا قِيلًا سَلَامًا سَلَامًا
Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.
56:27  وَأَصْحَابُ الْيَمِينِ مَا أَصْحَابُ الْيَمِينِ
Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
56:28  فِي سِدْرٍ مَّخْضُودٍ
(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.
56:29  وَطَلْحٍ مَّنضُودٍ
Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.
56:30  وَظِلٍّ مَّمْدُودٍ
Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.
56:31  وَمَاءٍ مَّسْكُوبٍ
Da wani ruwa mai gudãna.
56:32  وَفَاكِهَةٍ كَثِيرَةٍ
Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
56:33  لَّا مَقْطُوعَةٍ وَلَا مَمْنُوعَةٍ
Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.
56:34  وَفُرُشٍ مَّرْفُوعَةٍ
Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.
56:35  إِنَّا أَنشَأْنَاهُنَّ إِنشَاءً
Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.
56:36  فَجَعَلْنَاهُنَّ أَبْكَارًا
Sa'an nan Muka sanya su budurwai.
56:37  عُرُبًا أَتْرَابًا
Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
56:38  لِّأَصْحَابِ الْيَمِينِ
Ga mazõwa dãma.
56:39  ثُلَّةٌ مِّنَ الْأَوَّلِينَ
Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.
56:40  وَثُلَّةٌ مِّنَ الْآخِرِينَ
Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.
56:41  وَأَصْحَابُ الشِّمَالِ مَا أَصْحَابُ الشِّمَالِ
Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?
56:42  فِي سَمُومٍ وَحَمِيمٍ
Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.
56:43  وَظِلٍّ مِّن يَحْمُومٍ
Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.
56:44  لَّا بَارِدٍ وَلَا كَرِيمٍ
Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.
56:45  إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ
Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.
56:46  وَكَانُوا يُصِرُّونَ عَلَى الْحِنثِ الْعَظِيمِ
Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.
56:47  وَكَانُوا يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
56:48  أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ
"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
56:49  قُلْ إِنَّ الْأَوَّلِينَ وَالْآخِرِينَ
Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."
56:50  لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَاتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."
56:51  ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا الضَّالُّونَ الْمُكَذِّبُونَ
"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"
56:52  لَآكِلُونَ مِن شَجَرٍ مِّن زَقُّومٍ
"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."
56:53  فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
56:54  فَشَارِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ الْحَمِيمِ
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
56:55  فَشَارِبُونَ شُرْبَ الْهِيمِ
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
56:56  هَٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ الدِّينِ
Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.
56:57  نَحْنُ خَلَقْنَاكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ
Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?
56:58  أَفَرَأَيْتُم مَّا تُمْنُونَ
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
56:59  أَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُ أَمْ نَحْنُ الْخَالِقُونَ
Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?
56:60  نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ الْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,
56:61  عَلَىٰ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَالَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِي مَا لَا تَعْلَمُونَ
A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.
56:62  وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ النَّشْأَةَ الْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
56:63  أَفَرَأَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ
Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?
56:64  أَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُ أَمْ نَحْنُ الزَّارِعُونَ
Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?
56:65  لَوْ نَشَاءُ لَجَعَلْنَاهُ حُطَامًا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
56:66  إِنَّا لَمُغْرَمُونَ
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
56:67  بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"
56:68  أَفَرَأَيْتُمُ الْمَاءَ الَّذِي تَشْرَبُونَ
Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?
56:69  أَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ الْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ الْمُنزِلُونَ
Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?
56:70  لَوْ نَشَاءُ جَعَلْنَاهُ أُجَاجًا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ
Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?
56:71  أَفَرَأَيْتُمُ النَّارَ الَّتِي تُورُونَ
Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?
56:72  أَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَا أَمْ نَحْنُ الْمُنشِئُونَ
Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?
56:73  نَحْنُ جَعَلْنَاهَا تَذْكِرَةً وَمَتَاعًا لِّلْمُقْوِينَ
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
56:74  فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ
Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.
56:75  فَلَا أُقْسِمُ بِمَوَاقِعِ النُّجُومِ
To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.
56:76  وَإِنَّهُ لَقَسَمٌ لَّوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ
Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.
56:77  إِنَّهُ لَقُرْآنٌ كَرِيمٌ
Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
56:78  فِي كِتَابٍ مَّكْنُونٍ
A cikin wani littafi tsararre.
56:79  لَّا يَمَسُّهُ إِلَّا الْمُطَهَّرُونَ
Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.
56:80  تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَ
Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.
56:81  أَفَبِهَٰذَا الْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ
Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?
56:82  وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ
Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
56:83  فَلَوْلَا إِذَا بَلَغَتِ الْحُلْقُومَ
To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
56:84  وَأَنتُمْ حِينَئِذٍ تَنظُرُونَ
Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
56:85  وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ
Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.
56:86  فَلَوْلَا إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ
To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?
56:87  تَرْجِعُونَهَا إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ
Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.
56:88  فَأَمَّا إِن كَانَ مِنَ الْمُقَرَّبِينَ
To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,
56:89  فَرَوْحٌ وَرَيْحَانٌ وَجَنَّتُ نَعِيمٍ
Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.
56:90  وَأَمَّا إِن كَانَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ
Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,
56:91  فَسَلَامٌ لَّكَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ
Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.
56:92  وَأَمَّا إِن كَانَ مِنَ الْمُكَذِّبِينَ الضَّالِّينَ
Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,
56:93  فَنُزُلٌ مِّنْ حَمِيمٍ
Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.
56:94  وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ
Da ƙõnuwa da Jahĩm,
56:95  إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ الْيَقِينِ
Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.
56:96  فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.