aip_quran
Translation

  العربية              Hausa 

1. Surah Al-Fatiha
2. Surah Al-Baqara
3. Surah Aal-e-Imran
4. Surah An-Nisa
5. Surah Al-Maidah
6. Surah Al-Anam
7. Surah Al-Araf
8. Surah Al-Anfal
9. Surah At-Tawbah
10. Surah Yunus
11. Surah Hud
12. Surah Yusuf
13. Surah Ar-Rad
14. Surah Ibrahim
15. Surah Al-Hijr
16. Surah An-Nahl
17. Surah Al-Isra
18. Surah Al-Kahf
19. Surah Maryam
20. Surah Taha
21. Surah Al-Anbiya
22. Surah Al-Hajj
23. Surah Al-Muminun
24. Surah An-Nur
25. Surah Al-Furqan
26. Surah Ash-Shuara
27. Surah An-Naml
28. Surah Al-Qasas
29. Surah Al-Ankabut
30. Surah Ar-Rum
31. Surah Luqman
32. Surah As-Sajdah
33. Surah Al-Ahzab
34. Surah Saba
35. Surah Fatir
36. Surah Ya-Sin
37. Surah As-Saffat
38. Surah Sad
39. Surah Az-Zumar
40. Surah Ghafir
41. Surah Fussilat
42. Surah Ash-Shuraa
43. Surah Az-Zukhruf
44. Surah Ad-Dukhan
45. Surah Al-Jathiya
46. Surah Al-Ahqaf
47. Surah Muhammad
48. Surah Al-Fath
49. Surah Al-Hujurat
50. Surah Qaf
51. Surah Adh-Dhariyat
52. Surah At-Tur
53. Surah An-Najm
54. Surah Al-Qamar
55. Surah Ar-Rahman
56. Surah Al-Waqiah
57. Surah Al-Hadid
58. Surah Al-Mujadila
59. Surah Al-Hashr
60. Surah Al-Mumtahanah
61. Surah As-Saf
62. Surah Al-Jumuah
63. Surah Al-Munafiqun
64. Surah Al-Taghabun
65. Surah At-Talaq
66. Surah At-Tahrim
67. Surah Al-Mulk
68. Surah Al-Qalam
69. Surah Al-Haqqah
70. Surah Al-Maarij
71. Surah Nuh
72. Surah Al-Jinn
73. Surah Al-Muzzammil
74. Surah Al-Muddaththir
75. Surah Al-Qiyamah
76. Surah Al-Insan
77. Surah Al-Mursalat
78. Surah An-Naba
79. Surah An-Naziat
80. Surah Abasa
81. Surah At-Takwir
82. Surah Al-Infitar
83. Surah Al-Mutaffifin
84. Surah Al-Inshiqaq
85. Surah Al-Buruj
86. Surah At-Tariq
87. Surah Al-Ala
88. Surah Al-Ghashiyah
89. Surah Al-Fajr
90. Surah Al-Balad
91. Surah Ash-Shams
92. Surah Al-Layl
93. Surah Ad-Duhaa
94. Surah Ash-Sharh
95. Surah At-Tin
96. Surah Al-Alaq
97. Surah Al-Qadr
98. Surah Al-Bayyinah
99. Surah Az-Zalzalah
100. Surah Al-Adiyat
101. Surah Al-Qariah
102. Surah At-Takathur
103. Surah Al-Asr
104. Surah Al-Humazah
105. Surah Al-Fil
106. Surah Quraysh
107. Surah Al-Maun
108. Surah Al-Kawthar
109. Surah Al-Kafirun
110. Surah An-Nasr
111. Surah Al-Masad
112. Surah Al-Ikhlas
113. Surah Al-Falaq
114. Surah An-Nas

37. Surah As-Saffat

37:1  وَالصَّافَّاتِ صَفًّا
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
37:2  فَالزَّاجِرَاتِ زَجْرًا
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
37:3  فَالتَّالِيَاتِ ذِكْرًا
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
37:4  إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَاحِدٌ
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
37:5  رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِ
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
37:6  إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِ
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
37:7  وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍ
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
37:8  لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلَإِ الْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
37:9  دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
37:10  إِلَّا مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌ
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
37:11  فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا ۚ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍ
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
37:12  بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
37:13  وَإِذَا ذُكِّرُوا لَا يَذْكُرُونَ
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
37:14  وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَ
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
37:15  وَقَالُوا إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
37:16  أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
37:17  أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
37:18  قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَاخِرُونَ
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
37:19  فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
37:20  وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ الدِّينِ
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
37:21  هَٰذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
37:22  احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَ
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
37:23  مِن دُونِ اللَّهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطِ الْجَحِيمِ
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
37:24  وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَ
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
37:25  مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
37:26  بَلْ هُمُ الْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
37:27  وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
37:28  قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
37:29  قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
37:30  وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
37:31  فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
37:32  فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
37:33  فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
37:34  إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَ
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
37:35  إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَٰهَ إِلَّا اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
37:36  وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍ
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
37:37  بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
37:38  إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
37:39  وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
37:40  إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:41  أُولَٰئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ
Waɗannan sunã da abinci sananne.
37:42  فَوَاكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
37:43  فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
37:44  عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَ
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
37:45  يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
37:46  بَيْضَاءَ لَذَّةٍ لِّلشَّارِبِينَ
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
37:47  لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
37:48  وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌ
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
37:49  كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
37:50  فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
37:51  قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌ
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
37:52  يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنَ الْمُصَدِّقِينَ
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
37:53  أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَدِينُونَ
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
37:54  قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
37:55  فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاءِ الْجَحِيمِ
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
37:56  قَالَ تَاللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
37:57  وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَ
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
37:58  أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
37:59  إِلَّا مَوْتَتَنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
37:60  إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
37:61  لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ الْعَامِلُونَ
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
37:62  أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِ
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
37:63  إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَ
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
37:64  إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِ
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
37:65  طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُءُوسُ الشَّيَاطِينِ
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
37:66  فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
37:67  ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
37:68  ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
37:69  إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَ
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
37:70  فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
37:71  وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الْأَوَّلِينَ
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
37:72  وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
37:73  فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَ
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
37:74  إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:75  وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَ
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
37:76  وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
37:77  وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمُ الْبَاقِينَ
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
37:78  وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
37:79  سَلَامٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَ
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
37:80  إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:81  إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
37:82  ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
37:83  وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَ
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
37:84  إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
37:85  إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَ
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
37:86  أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللَّهِ تُرِيدُونَ
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
37:87  فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
37:88  فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِ
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
37:89  فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٌ
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
37:90  فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَ
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
37:91  فَرَاغَ إِلَىٰ آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
37:92  مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
37:93  فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِ
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
37:94  فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَ
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
37:95  قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
37:96  وَاللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
37:97  قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِ
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
37:98  فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الْأَسْفَلِينَ
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
37:99  وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهْدِينِ
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
37:100  رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
37:101  فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلَامٍ حَلِيمٍ
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
37:102  فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَىٰ فِي الْمَنَامِ أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللَّهُ مِنَ الصَّابِرِينَ
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
37:103  فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِ
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
37:104  وَنَادَيْنَاهُ أَن يَا إِبْرَاهِيمُ
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
37:105  قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:106  إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْبَلَاءُ الْمُبِينُ
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
37:107  وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
37:108  وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
37:109  سَلَامٌ عَلَىٰ إِبْرَاهِيمَ
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
37:110  كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:111  إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
37:112  وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَ
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
37:113  وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰ إِسْحَاقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌ
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
37:114  وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
37:115  وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
37:116  وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
37:117  وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَ
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
37:118  وَهَدَيْنَاهُمَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
37:119  وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِي الْآخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
37:120  سَلَامٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
37:121  إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:122  إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
37:123  وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
37:124  إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
37:125  أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ الْخَالِقِينَ
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
37:126  اللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
37:127  فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
37:128  إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:129  وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
37:130  سَلَامٌ عَلَىٰ إِلْ يَاسِينَ
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
37:131  إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:132  إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
37:133  وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ الْمُرْسَلِينَ
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
37:134  إِذْ نَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
37:135  إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
37:136  ثُمَّ دَمَّرْنَا الْآخَرِينَ
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
37:137  وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
37:138  وَبِاللَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
37:139  وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
37:140  إِذْ أَبَقَ إِلَى الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
37:141  فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ الْمُدْحَضِينَ
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
37:142  فَالْتَقَمَهُ الْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌ
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
37:143  فَلَوْلَا أَنَّهُ كَانَ مِنَ الْمُسَبِّحِينَ
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
37:144  لَلَبِثَ فِي بَطْنِهِ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
37:145  فَنَبَذْنَاهُ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ سَقِيمٌ
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
37:146  وَأَنبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍ
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
37:147  وَأَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ مِائَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
37:148  فَآمَنُوا فَمَتَّعْنَاهُمْ إِلَىٰ حِينٍ
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
37:149  فَاسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ الْبَنَاتُ وَلَهُمُ الْبَنُونَ
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
37:150  أَمْ خَلَقْنَا الْمَلَائِكَةَ إِنَاثًا وَهُمْ شَاهِدُونَ
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
37:151  أَلَا إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
37:152  وَلَدَ اللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَ
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
37:153  أَصْطَفَى الْبَنَاتِ عَلَى الْبَنِينَ
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
37:154  مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
37:155  أَفَلَا تَذَكَّرُونَ
Shin, bã ku tunãni?
37:156  أَمْ لَكُمْ سُلْطَانٌ مُّبِينٌ
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
37:157  فَأْتُوا بِكِتَابِكُمْ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
37:158  وَجَعَلُوا بَيْنَهُ وَبَيْنَ الْجِنَّةِ نَسَبًا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ الْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
37:159  سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
37:160  إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:161  فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
37:162  مَا أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَاتِنِينَ
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
37:163  إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ الْجَحِيمِ
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
37:164  وَمَا مِنَّا إِلَّا لَهُ مَقَامٌ مَّعْلُومٌ
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
37:165  وَإِنَّا لَنَحْنُ الصَّافُّونَ
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
37:166  وَإِنَّا لَنَحْنُ الْمُسَبِّحُونَ
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
37:167  وَإِن كَانُوا لَيَقُولُونَ
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
37:168  لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنَ الْأَوَّلِينَ
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
37:169  لَكُنَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
37:170  فَكَفَرُوا بِهِ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
37:171  وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا الْمُرْسَلِينَ
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
37:172  إِنَّهُمْ لَهُمُ الْمَنصُورُونَ
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
37:173  وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ الْغَالِبُونَ
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
37:174  فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
37:175  وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
37:176  أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
37:177  فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَاءَ صَبَاحُ الْمُنذَرِينَ
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
37:178  وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
37:179  وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
37:180  سُبْحَانَ رَبِّكَ رَبِّ الْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
37:181  وَسَلَامٌ عَلَى الْمُرْسَلِينَ
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
37:182  وَالْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.